Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kashe Naira Biliyan 1.8 Wajen Hayar Ofis a Shekaru Uku – HoCS

Daga Willies Ugo | Gombe

Gombe – yuni 2nd 2025

Gwamnatin Jihar Gombe ta kashe sama da Naira biliyan 1.8 wajen hayar ofisoshi a cikin shekaru uku da suka wuce, sakamakon rashin ingantacciyar Ma’aikatar Gwamnati (State Secretariat), a cewar Shugaban Ma’aikata na Jihar, Ahmed Kasimu Abdullahi.

Ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da manema labarai a Gombe, inda ya yaba wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa kudurinsa na kawo karshen matsalar rashin wadatattun ofisoshi ga Ma’aikatun Gwamnati da Sassa (MDAs) a jihar.

Abdullahi ya ce gwamnatin jihar ta yanke shawarar gina sabon ginin Ma’aikatar Gwamnati na zamani da za a kashe Naira biliyan 68.58 a kai — matakin da ya ce ya dace kuma ya zo a kan kari, shekaru kusan talatin bayan kirkirowar jihar a shekarar 1996.

Gwamnati ta kashe akalla Naira miliyan 600 a kowace shekara cikin shekaru ukun nan da suka wuce wajen haya. Wannan ba ya hada da biliyoyin naira da gwamnatocin baya suka kashe a irin wannan tsari,” in ji shi.

Wani Aiki da Aka Dade Ana Jira

Ya bayyana cewa tsohon ginin Ma’aikatar Gwamnatin da ake amfani da shi yanzu ba shi da isasshen sarari tunda tun da farko ba don dindindin aka gina shi ba. Sakamakon haka, da dama daga cikin ma’aikatun gwamnati suna aiki ne daga wurare daban-daban da aka haya ko kuma marasa inganci.

A cewarsa, gazawar gwamnatocin baya wajen fifita gina ingantaccen ginin ma’aikata ya hana ingantaccen aiki da gudanarwa a cikin gwamnati.

Gina sabon ginin Ma’aikatar Gwamnati wata babbar nasara ce. Za a gina shi ne bisa ka’idodin zamani, kuma zai yi wa al’umma amfani na dogon lokaci,” in ji shi.

Tsarin Aikin da Lokacin Kammalawa

An bai wa kamfanin Datum Construction Nigeria Limited aikin, wanda zai kunshi rassa hudu, kowanne zai dauki ma’aikatu hudu, banda Ofishin Shugaban Ma’aikata da za a ware masa wurin musamman.

Abdullahi ya kara da cewa wannan aiki na daga cikin shirin Three Arms Zone, wanda zai hada da Majalisar Dokokin Jihar da kuma Bangaren Shari’a na jihar.

Ana sa ran aikin zai kammala cikin makonni 102.

Inganta Aikin Gwamnati

Shugaban Ma’aikatan ya bayyana cewa wannan aiki zai taimaka wajen inganta gudanar da ayyukan gwamnati, rage kashe kudin haya da kuma samar da daidaito da tsaro wajen gudanar da ayyuka a ofisoshin gwamnati.

Wannan aiki ne na tarihi da ke nuna hangen nesa na Gwamna wajen gyara tsarin gwamnati da ci gaban gina ababen more rayuwa,” in ji shi.

Don samun ƙarin sabbin labarai, ku biyo mu a:
X (Twitter): @TheNewspointer
WhatsApp, Instagram, da Facebook: @TheNewspointer
📞 Tuntuɓe Mu:
✉️ Imel:
ishakudanzumi1@gmail.com
humtarosamson@gmail.com
📱 Lambar Waya:
0707 114 4444
0813 846 5350
🖋️ Editocin Yanar Gizo:
Prince Hassan Danzumi Ishaku / Humtaro S. Humtaro
© 2024 TheNewspointer.com.ng – An tanada duk haƙƙin mallaka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *